'Yan sanda sun kama Angon da ya yi wa Amaryarsa sanadin mutuwa

Rundunar ‘yan sanda a jihar Legas ta ce ta kama wani Ango dan shekara 30, mai suna


Motunrayo Olaniyi, bisa zarginsa da daba wa matarsa ​​mai suna Olajumoke ‘yar shekara 25 wuka har lahira.


Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Benjamin Hundeyin, ya tabbatar da faruwar lamarin ga Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ranar Asabar a Legas.


 Ya ce lamarin ya faru ne a ranar Juma’a da misalin karfe 1:00 na rana a Amazing Grace Estate, Elepe, a yankin Ikorodu na jihar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp