Kungiyar kwadago ta Najeriya NLC ta bukaci gwamnatin Nijeriya da ta rage karin farashin man fetur da tayi a yan kwanakin nan.
Bayanin hakan na a cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar kwadagon ta NLC ya fitar, Joe Ajaero, a Abuja, yana mai cewa karin kudin ya kara ta’azzara talauci a duka fadin kasar nan, kuma babu wani fa’ida ta zahiri tattare da shi.
Sabon karin farashin man fetur din ya kai Naira 1,030 kan kowace lita a gidajen mai na kamfanin NNPCL mai kula da harkokin mai a Nijeriya.
Category
Labarai