Muna aiki tukuru don shawo kan matsalar wutar lantarki da Arewacin Nijeriya ke fuskanta - Kamfanin TCN


Layin wuta

Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya ya rawaito cewa TCN ya ce ma'aikatan su sun gano dalilin da ya haddasa matsalar wutar lantarki a layin Ugwuaji-Apir mai nauyin kilo 330 (kV).


Babban jami'in hulda da jama’a na TCN, Ndidi Mbah, ya ce an gano matsalar ne a yankin Igumale da ke Jihar Binuwai, a cewarsa, yankin da aka samu matsalar, an gano yana da karfin 330kv a cikin dajin Igumale da ke jihar Benuwe.


Ya kara da cewa jami'an TCN na aiki tukuru domin shawo kan matsalar wutar lantarki da ta addabi wasu yankunan.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp