Mazauna unguwanni da dama a Ado Ekiti da wasu garuruwan jihar Ekiti sun shiga cikin duhu yayin da guguwar ruwan sama ta lalata turakun lantarki



Wuraren da abin ya shafa sun hada da Ajebamidele, Omisanjana da Atlas duk a Ado Ekiti, Ikere Ekiti, Ise Ekiti da Emure Ekiti.                         

                             

Ruwan sama kamar da bakin kwarya da ya mamaye unguwannin a karshen makon da ya gabata, ya kawo cikas ga harkokin zirga-zirga, zamantakewa da tattalin arzikin yankin.


Ruwan saman ya yi awon gaba da sandunan turakun lantarki a kusa da Deeper Life Campground a Ajebamidele, unguwar da ke da yawan jama'a a babban birnin jihar.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp