Matatar man Dangote ta sahale wa 'yan kasuwa su rika sayen mai kai tsaye ba tare da sa hannun NNPCL ba



Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPC ya kawo karshen yarjejeniyar sayen mai da matatar Dangote a hukumance, inda ta bude kasuwa ga sauran ‘yan kasuwa su sayi mai kai tsaye daga matatar.

Wannan matakin na nuni da cewa kamfanin na NNPC ba zai cigaba da zama dillali tsakanin matatar da 'yan kasuwa ba, da hakan zai bai ‘yan kasuwa damar tattaunawa kan farashi kai tsaye da matatar Dangote.

Wannan sauyin ya zo daidai da tsarin kasuwanci, inda matatun mai za su iya sayar da man kai tsaye ga 'yan kasuwa a duk lokacin da suka bukata.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp