Mabarata na nuna rashin jin dadinsu bisa yadda hukumomi a Abuja ke ci gaba da kama su

Masu Bara a Abuja



City & Crime ta rawaito cewa ministan birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya umarci jami’an gwamnatin da su tsafta ce babban birnin Abuja baki daya.Tun da farko dai ya baiwa mabarata zuwa ranar Lahadin da ta gabata da su fice daga titunan Abuja ko kuma a kama su.

Da suke mayar da martani a ranar laraba, wasu mabarata, masu bukata ta musamman, sun nuna rashin amincewarsu da matakin da aka dauka, inda suka bayyana damuwarsu a lokacin da suka ziyarci babban ofishin Daily Trust a Abuja.

Auwal I. Alhassan, wanda ya yi magana a madadinsu, ya soki mahukunta a birnin tarayya da rashin yin hulda da su, ko kuma magance korafe-korafensu kafin a ba da umarnin korar su. Ya ce, abin takaici ne mahukuntan su ce sai sun koresu daga inda suke duk da suna da hakkin rayuwa a ko ina.

Ya kara da cewa, baya ga kungiyar SERAP, babu wata kungiya mai zaman kanta, ko kungiyoyin farar hula, ko kungiyoyin addini da suka kai musu dauki. Alhassan ya yi ikirarin cewa wadanda aka kama suna rayuwa ne a cikin mawuyacin hali a gidan gyaran hali da ke Bwari, ba su da abinci, ruwa, da kuma kula da lafiya.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp