Gwamnatin tarayya ta sha alwashin kawar da yan bindiga a Arewa maso Yamma

Ministan tsaron Nijeriya, Mohammed Badaru Abubakar

Ministan tsaron Nijeriya, Mohammed Badaru Abubakar, ya sake jaddada aniyar gwamnatin tarayya na magance matsalar rashin tsaro a fadin kasa baki daya.

Ministan ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai wa Gwamna Uba Sani ziyarar ban girma a gidan gwamnatin Sir Kashim Ibrahim da ke Kaduna a wani rangadin da ya ke yi a shiyyar Arewa maso Yamma.

Ziyarar dai na da nufin kammala shirye-shiryen kaddamar da shirin ‘Operation Fansan Yamma' domin magance matsalar rashin tsaro a yankin.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp