Majalisar wakilai ta umarci JAMB da ta tura N3bn ga asusun gwamnatin tarayya

 


Majalisar wakilai ta umurci hukumar shirya jarabawar shiga jami’a ta JAMB da ta tura naira biliyan 3.602 ga asusun hadakar kudaden shiga na gwamnatin tarayya.

Shugaban kwamitin kula da harkokin jama’a, Bamidele Salam ne ya bayar da wannan umarni a yayin wani zaman bincike ga hukumar a Abuja, wanda hukumar kula da kasafin kudi ta (FRC) ta bukata.

Salam ya ce wannan lamari ne na doka, kuma ba shi da alaka da banbancin kashi 25 da kashi 50 bisa 100 kamar yadda hukumar JAMB ta ce.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp