Naja'atu Mohd, Usman Yusuf, Umar Ardo, Salihu Lukman sun goyi bayan matasa kan zanga-zanga

 

MUNA TARE DA MATASAN MU

Wannan sanarwar ce ga manema labaru a kan zanga-zangar da ake shirin yi, da aka fitar da ita a ranar 31 ga watan Yuli wadda dattajan arewacin Najeriya da suka hada da Professor Usman Yusuf da Naja’atu Muhammad da Malam Salihu Lukman da Dr. Ardo Umar suka fitar a birnin Abuja.  

-------

Mu dattawan Arewa kuma ginshikai da ke da ruwa da tsaki a ƙasar nan muka yi wannan rubutu domin tsayar da matsaya a kan babban lamari da ya shafe mu duka.

 

Kamar yadda kuka sani, ƙasarmu ta dade tana fama da matsaloli ba 'yan kaɗan ba ɓangaren rashin tsaro, da tsananin talauci, da tsananin yunwa da jahilci  da rashin aikin yi, da cututtuka da tsananin tsadar rayuwa, da duk rashin shugabanci na gari da rashawa a ofisoshi ne gwamnati suka haddasa su.

 

Muna sane cewa babbar manufar dukkan wata gwamnati ita ce kare rayuka da dukiyar jama'a da kyautata jin dadin al'ummar kasa. Duk  gwamnatin da ba ta iya samar wa al'ummarta wadannan muhimman haƙƙoƙi nasu to ta rasa huruminta na ci gaba da kasancewa a madafun iko, kuma ko shakka babu za ta gamu da fushin 'yan ƙasa. Saboda haka za ta iya ci gaba da kasancewa a kan mulki ne ba da fatan alheri daga jama'a ba.

 

Da alama yanayin da ake ciki ke nan a Najeriya, inda ƙasarmu, abar ƙaunarmu Nijeriya, ta dosa ke nan.

Shekaru da dama gwamnatocin da suka gabata a dukkan matakai, ciki har da gwamnatoci da ke ci a yanzu, sun gaza samar da shugabancin da ake buƙata.

 

Saboda haka aka jefa 'yan Nijeriya cikin mawuyacin hali, na rashin sanin inda rayuwarsu ta dosa, ga ƙunci da sauransu musamman matasa.

 

Domin matasa su bayyana buƙatunsu kan tsadar rayuwa, da matsalar tsaro, da lalacewar lamura, suka sa matasan Nijeriya suka yanke shawarar gudanar da zanga-zanga ta ƙasa baki-ɗaya daga 1 zuwa 10 ga watan Agusta.

 

Saboda haka muka rubuta wannan sanarwa ta musamman domin bayyana matsayinmu a game da wannan zanga-zanga da matasa suka tsara da kuma halin da gwamnati take nunawa a kan zanga-zangar.

 

Da farko muna so mu jaddada kariyar da tsarin mulki ya ba kowanne ɗan ƙasa a 'yancin da yake da shi na yin taro da kuma yin zanga-zanga.

 

Har ila yau muna jaddada cewa dalilan da suka haddasa zanga-zangar dalilai ne masu ƙwari.


Saboda haka muke bayyanawa ɓaro-ɓaro cewa muna tare da matasanmu a wannan gwagwarmaya tasu ta aiki da 'yancin da suke da shi na gudanar da zanga-zanga.


Na biyu muna kira ga gwamnatin tarayya ta zama mai sanin ya kamata wajen warware wannan matsala idan har tana so ta warware cikin ruwan sanyi da kauce wa dukkan wata matsala da ke tattare da gagarumar zanga-zanga. Saboda haka muke ba gwamnati shawarar ta hanzarta ɗaukar waɗannan matakan:

 

 1. Tattaunawa: Gano shugabannin matasan da masu zanga-zangar tare da ganawa da su kai tsaye domin fahimtar ƙorafe-ƙorafensu da kuma magance musu su. Ɗora wa wasu wannan aiki kamar irin su sarakuna, da shugabannin addini, da shugabannin kwadago da na farar hula ba zai yi aiki ba.

 

Amfani da ƙarfin tuwo wajen tursasa wa masu zanga-zangar zai ƙara sa yanayin da ake ciki ya ƙara ta'azzara ne. Mun dai ga yadda zanga-zangar EndSARS ta wanye.

 

2. Aiwatar da sauye-sauye: A duba buƙatun masu zanga-zangar tsakani da Allah ta hanyar aiwatar da sauye-sauye masu ma'ana, da nuna fata ta gari da dukufa ga canji.

 

3. Ba da goyon baya ga karfafa matasa: A zuba jari ga tsare-tsare na ci gaban matasa, da iliminsu da dabaru na bunƙasa kasuwancinsu.

 

4. Bunƙasa ci gaban tattalin arziki: Aiwatar da tsare-tsare da za su kyautata ilahirin ci-gaban tattalin arzikin ƙasa.

 

5. Kyautata shugabanci: Gaskiya da riƙon amana da damawa da kowa a sha'anin shugabanci, maimakon shugabanci na son- kai da-baba-kere, da magance rashawa da tabbatar da dama iri guda ga dukkan 'yan ƙasa.

 

6. Tabbatar da tsaro: A tabbatar da jami'an tsaro na ƙasa sun mutunta 'yancin da masu zanga-zangar suke da shi ta hanyar ƙyale su, su gudanar da taronsu cikin ruwan sanyi ba tare da musu katsalandan ba, ko tursasa musu ko cin zarafinsu ba, tare da kare su daga dukkan wata illa ko rauni.

 

7. Shugabanci abin koyi: Ya kamata gwamnati da shugabanninta su nuna shugabanci abin koyi, nuna sadaukar da kai, da kima, da martaba domin cusa ƙauna da amincewa.

 

A matsayinsa na wanda shi da kansa ya jagoranci zanga-zanga daban-daban daga lokacin kungiyar NADECO zuwa shekara ta 2014, Shugaba Tinubu ya fi kowa sanin darajar zanga-zanga.

 

Ga su kuma matasa masu zanga-zanga, muna so mu tabbatar muku cewa mun fahimta tare da ba da goyon bayan wannan shawara da kuka yanke ta aiki da 'yancin da kundin tsarin mulki ya ba ku ta gudanar da zanga-zanga ta lumana domin neman shugabanci na gari da gaskiya daga shugabanku.

 

Mun yi imanin cewa wannan mataki ne halastacce kuma matakin da ya wajaba domin kyautata alƙiblarku da tabbatar da Nijeriya ta mana daɗi gaba ɗayanmu.

 

A matsayinmu na dattawa, a lokacin da muke tafiya kafaɗa-da-kafada da ku a kan wannan, muna kira a gare ku, ku ci gaba da kasancewa masu zaman lafiya da kiyaye doka a lokacin wannan zanga-zanga, da kauce wa dukkan wani abu da zai iya zamewa tashin hankali, ko illa, ko ɓarna ko barazana ga zaman lafiya.

 

Har ila yau muna kira gare ku, ku amince da tattaunawa idan gwamnati ta nemi yin haka da ku wajen magance ainihin musabbabin ɓacin ranku.

 

Ta hanyar ɗaukar waɗannan matakai, gwamnati tana iya magance waɗannan matsaloli da suka yi sanadiyyar zanga-zangar, da rage zaman ɗar-ɗar da samar da kyakkyawar makoma da kauce wa dukkan wata tashin-tashina.

 

Muna kira ga shugabanninmu da gwamnatoci a kowanne mataki su zama masu sauraren koke-koken jama'a, su kuma  mutunta 'yancin kowanne ɗan ƙasa na bayyana ra'ayinsa ba tare da wata tsangwama ba, kamar yadda kundin tsarin mulki na shekarar 1999 ya tanadar.

 

Mun yi imanin cewa idan muka hada ƙarfi, za mu iya samar da ƙasa da za ta yi wa kowa daɗi, ba tare da wani bambanci na shekara, ko ƙabila, ko matsayi na zamantakewa da tattalin arziki ba.

 

Muna godiya. Sakonmu ke nan a yau, mune naku

 

 Farfesa Usman Yusuf da  Hajiya Naja'atu Muhammad

Da Malam Salihu Lukman da kuma Dakta Umar Ardo

 

 


Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp