'Yan majalisa ne suka matsa wa gwamnatin tarayya lamba har ta sanya hannu kan SAMOA - Ministan Tinubu


Jaridar Premium Times ta ce ta samu wata wasika daga Majalisar Dokoki ta kasa zuwa ga Ministan Kasafin Kudi da Tsare-tsare na kasa, Atiku Bagudu, inda ya nemi gwamnati ta sanya hannu kan yarjejeniyar.

Majalisar ta bukaci gwamnati da ta dakatar da aiwatar da yarjejeniyar a ranar Alhamis, har sai kwamitin ta ya gudanar da bincike akai.

Sai dai wasikar ta nuna sabanin matsayin majalisar kan yarjejeniyar.

A cikin wasikar mai dauke da kwanan watan 9 ga Mayu 2024, kuma Muhammed Argungu ya sanya wa hannu, Majalisar ta bukaci ministan da ya rattaba hannu kan yarjejeniyar ga kungiyar kasashen Afirka da Caribbean da Pacific da Tarayyar Turai.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp