Cutar mashako ta yi wa yara 4 sanadin mutuwa a Kano

 


An samu bullar wata sabuwar cutar mashako inda ta kashe yara hudu a wasu kauyukan karamar hukumar Mingibir ta jihar Kano.


Rahotannin sun ce karin wasu mutanen 28 na kwance a asibiti kamar yadda wata sanarwa da jami’in yada labarai na karamar hukumar Tasiu Dadin-Duniya ya fitar a ranar Alhamis, inji rahoton Punch.


A cewar sanarwar, yaran sun kamu da cutar ne a kauyukan Kwarkiya, Kuru, Kunya da Minjibir dake karamar hukumar Minjibir.

Post a Comment

Previous Post Next Post

Kasance da DCL Hausa a kan manhajar WhatsApp